Hausa
Surah Al-Fatihah ( The Opening ) - Aya count 7
بِسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ ﰀ ﴿١﴾
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ ﰁ ﴿٢﴾
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ ﰂ ﴿٣﴾
مَٰلِكِ يَوۡمِ ٱلدِّينِ ﰃ ﴿٤﴾
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
إِيَّاكَ نَعۡبُدُ وَإِيَّاكَ نَسۡتَعِينُ ﰄ ﴿٥﴾
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
ٱهۡدِنَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ ﰅ ﴿٦﴾
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
صِرَٰطَ ٱلَّذِينَ أَنۡعَمۡتَ عَلَيۡهِمۡ غَيۡرِ ٱلۡمَغۡضُوبِ عَلَيۡهِمۡ وَلَا ٱلضَّآلِّينَ ﰆ ﴿٧﴾
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.