Hausa
Surah Al-'adiyat ( Those That Run ) - Aya count 11
وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا ﰀ ﴿١﴾
Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.
فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا ﰁ ﴿٢﴾
Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.
فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا ﰂ ﴿٣﴾
Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.
فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا ﰃ ﴿٤﴾
Sai su motsar da ƙũra game da shi.
فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا ﰄ ﴿٥﴾
Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.
إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٞ ﰅ ﴿٦﴾
Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.
وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٞ ﰆ ﴿٧﴾
Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.
وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلۡخَيۡرِ لَشَدِيدٌ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.
۞ أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ ﰈ ﴿٩﴾
Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.
وَحُصِّلَ مَا فِي ٱلصُّدُورِ ﰉ ﴿١٠﴾
Aka bayyana abin da ke cikin zukata.
إِنَّ رَبَّهُم بِهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّخَبِيرُۢ ﰊ ﴿١١﴾
Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?