The best companion that never bores
Surah Al-Fil ( The Elephant )

Hausa

Surah Al-Fil ( The Elephant ) - Aya count 5

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ ﰀ ﴿١﴾

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?

أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ ﰁ ﴿٢﴾

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?

وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ ﰂ ﴿٣﴾

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.

تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ ﰃ ﴿٤﴾

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.

فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفٖ مَّأۡكُولِۭ ﰄ ﴿٥﴾

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?