Hausa
Surah Al-Fil ( The Elephant ) - Aya count 5
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ ﰀ ﴿١﴾
Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?
أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ ﰁ ﴿٢﴾
Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?
وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ ﰂ ﴿٣﴾
Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.
تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ ﰃ ﴿٤﴾
Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.
فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفٖ مَّأۡكُولِۭ ﰄ ﴿٥﴾
Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?