The best companion that never bores
Surah Al-Qiyamah ( The Resurrection )

Hausa

Surah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) - Aya count 40

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ ﰀ ﴿١﴾

Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ ﰁ ﴿٢﴾

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ ﰂ ﴿٣﴾

Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ ﰃ ﴿٤﴾

Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ ﰄ ﴿٥﴾

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ ﰅ ﴿٦﴾

Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ ﰆ ﴿٧﴾

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ ﰇ ﴿٨﴾

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ ﰈ ﴿٩﴾

Aka tãra rãnã da watã

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ ﰉ ﴿١٠﴾

Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

كَلَّا لَا وَزَرَ ﰊ ﴿١١﴾

A'aha! bãbu mafaka.

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ ﰋ ﴿١٢﴾

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ ﰌ ﴿١٣﴾

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ ﰍ ﴿١٤﴾

Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ ﰎ ﴿١٥﴾

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ ﰏ ﴿١٦﴾

Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ ﰐ ﴿١٧﴾

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ ﰑ ﴿١٨﴾

To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ ﰒ ﴿١٩﴾

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ ﰓ ﴿٢٠﴾

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

وَتَذَرُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ ﰔ ﴿٢١﴾

Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاضِرَةٌ ﰕ ﴿٢٢﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٞ ﰖ ﴿٢٣﴾

Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذِۭ بَاسِرَةٞ ﰗ ﴿٢٤﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

تَظُنُّ أَن يُفۡعَلَ بِهَا فَاقِرَةٞ ﰘ ﴿٢٥﴾

Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِيَ ﰙ ﴿٢٦﴾

A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

وَقِيلَ مَنۡۜ رَاقٖ ﰚ ﴿٢٧﴾

kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلۡفِرَاقُ ﰛ ﴿٢٨﴾

Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

وَٱلۡتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ ﰜ ﴿٢٩﴾

Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمَسَاقُ ﰝ ﴿٣٠﴾

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ ﰞ ﴿٣١﴾

To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ﰟ ﴿٣٢﴾

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ ﰠ ﴿٣٣﴾

Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰ ﰡ ﴿٣٤﴾

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

ثُمَّ أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰٓ ﰢ ﴿٣٥﴾

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَن يُتۡرَكَ سُدًى ﰣ ﴿٣٦﴾

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ ﰤ ﴿٣٧﴾

Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ ﰥ ﴿٣٨﴾

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ ﰦ ﴿٣٩﴾

Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ ﰧ ﴿٤٠﴾

Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?