Hausa
Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya count 46
وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرۡقٗا ﰀ ﴿١﴾
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشۡطٗا ﰁ ﴿٢﴾
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبۡحٗا ﰂ ﴿٣﴾
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبۡقٗا ﰃ ﴿٤﴾
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَٱلۡمُدَبِّرَٰتِ أَمۡرٗا ﰄ ﴿٥﴾
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﰅ ﴿٦﴾
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتۡبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﰆ ﴿٧﴾
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٞ يَوۡمَئِذٖ وَاجِفَةٌ ﰇ ﴿٨﴾
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبۡصَٰرُهَا خَٰشِعَةٞ ﰈ ﴿٩﴾
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرۡدُودُونَ فِي ٱلۡحَافِرَةِ ﰉ ﴿١٠﴾
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمٗا نَّخِرَةٗ ﰊ ﴿١١﴾
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُواْ تِلۡكَ إِذٗا كَرَّةٌ خَاسِرَةٞ ﰋ ﴿١٢﴾
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ ﰌ ﴿١٣﴾
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﰍ ﴿١٤﴾
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ ﰎ ﴿١٥﴾
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى ﰏ ﴿١٦﴾
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﰐ ﴿١٧﴾
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﰑ ﴿١٨﴾
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ ﰒ ﴿١٩﴾
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ ﰓ ﴿٢٠﴾
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﰔ ﴿٢١﴾
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ ﰕ ﴿٢٢﴾
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﰖ ﴿٢٣﴾
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ ﰗ ﴿٢٤﴾
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ ﰘ ﴿٢٥﴾
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ ﰙ ﴿٢٦﴾
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا ﰚ ﴿٢٧﴾
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا ﰛ ﴿٢٨﴾
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا ﰜ ﴿٢٩﴾
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ ﰝ ﴿٣٠﴾
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا ﰞ ﴿٣١﴾
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا ﰟ ﴿٣٢﴾
مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ ﰠ ﴿٣٣﴾
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ ﰡ ﴿٣٤﴾
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ ﰢ ﴿٣٥﴾
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ﰣ ﴿٣٦﴾
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ﰤ ﴿٣٧﴾
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا ﰥ ﴿٣٨﴾
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ ﰦ ﴿٣٩﴾
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ ﰧ ﴿٤٠﴾
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ ﰨ ﴿٤١﴾
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا ﰩ ﴿٤٢﴾
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ ﰪ ﴿٤٣﴾
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ ﰫ ﴿٤٤﴾
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا ﰬ ﴿٤٥﴾
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا ﰭ ﴿٤٦﴾
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.