Hausa
Surah Abasa ( He frowned ) - Aya count 42
عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ ﰀ ﴿١﴾
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
أَن جَآءَهُ ٱلۡأَعۡمَىٰ ﰁ ﴿٢﴾
Sabõda makãho yã je masa.
وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ ﰂ ﴿٣﴾
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
أَوۡ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكۡرَىٰٓ ﰃ ﴿٤﴾
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
أَمَّا مَنِ ٱسۡتَغۡنَىٰ ﰄ ﴿٥﴾
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ ﰅ ﴿٦﴾
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
وَمَا عَلَيۡكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ ﰆ ﴿٧﴾
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسۡعَىٰ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
وَهُوَ يَخۡشَىٰ ﰈ ﴿٩﴾
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
فَأَنتَ عَنۡهُ تَلَهَّىٰ ﰉ ﴿١٠﴾
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
كَلَّآ إِنَّهَا تَذۡكِرَةٞ ﰊ ﴿١١﴾
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﰋ ﴿١٢﴾
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
فِي صُحُفٖ مُّكَرَّمَةٖ ﰌ ﴿١٣﴾
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
مَّرۡفُوعَةٖ مُّطَهَّرَةِۭ ﰍ ﴿١٤﴾
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
بِأَيۡدِي سَفَرَةٖ ﰎ ﴿١٥﴾
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
كِرَامِۭ بَرَرَةٖ ﰏ ﴿١٦﴾
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
قُتِلَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَآ أَكۡفَرَهُۥ ﰐ ﴿١٧﴾
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
مِنۡ أَيِّ شَيۡءٍ خَلَقَهُۥ ﰑ ﴿١٨﴾
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
مِن نُّطۡفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ ﰒ ﴿١٩﴾
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ ﰓ ﴿٢٠﴾
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقۡبَرَهُۥ ﰔ ﴿٢١﴾
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ ﰕ ﴿٢٢﴾
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
كَلَّا لَمَّا يَقۡضِ مَآ أَمَرَهُۥ ﰖ ﴿٢٣﴾
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ ﰗ ﴿٢٤﴾
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
أَنَّا صَبَبۡنَا ٱلۡمَآءَ صَبّٗا ﰘ ﴿٢٥﴾
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
ثُمَّ شَقَقۡنَا ٱلۡأَرۡضَ شَقّٗا ﰙ ﴿٢٦﴾
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا حَبّٗا ﰚ ﴿٢٧﴾
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
وَعِنَبٗا وَقَضۡبٗا ﰛ ﴿٢٨﴾
وَزَيۡتُونٗا وَنَخۡلٗا ﰜ ﴿٢٩﴾
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
وَحَدَآئِقَ غُلۡبٗا ﰝ ﴿٣٠﴾
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
وَفَٰكِهَةٗ وَأَبّٗا ﰞ ﴿٣١﴾
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
مَّتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ ﰟ ﴿٣٢﴾
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ ﰠ ﴿٣٣﴾
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ ﰡ ﴿٣٤﴾
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ ﰢ ﴿٣٥﴾
وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ ﰣ ﴿٣٦﴾
لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ ﰤ ﴿٣٧﴾
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ ﰥ ﴿٣٨﴾
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ ﰦ ﴿٣٩﴾
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ ﰧ ﴿٤٠﴾
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ ﰨ ﴿٤١﴾
أُوْلَٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ ﰩ ﴿٤٢﴾
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).