Hausa
Surah At-Takwir ( The Overthrowing ) - Aya count 29
إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ ﰀ ﴿١﴾
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ ﰁ ﴿٢﴾
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ سُيِّرَتۡ ﰂ ﴿٣﴾
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا ٱلۡعِشَارُ عُطِّلَتۡ ﰃ ﴿٤﴾
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا ٱلۡوُحُوشُ حُشِرَتۡ ﰄ ﴿٥﴾
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ سُجِّرَتۡ ﰅ ﴿٦﴾
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ ﰆ ﴿٧﴾
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ ﰈ ﴿٩﴾
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ ﰉ ﴿١٠﴾
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتۡ ﰊ ﴿١١﴾
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا ٱلۡجَحِيمُ سُعِّرَتۡ ﰋ ﴿١٢﴾
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ ﰌ ﴿١٣﴾
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ ﰍ ﴿١٤﴾
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ ﰎ ﴿١٥﴾
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ ﰏ ﴿١٦﴾
وَٱلَّيۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ ﰐ ﴿١٧﴾
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ ﰑ ﴿١٨﴾
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ ﰒ ﴿١٩﴾
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي ٱلۡعَرۡشِ مَكِينٖ ﰓ ﴿٢٠﴾
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
مُّطَاعٖ ثَمَّ أَمِينٖ ﰔ ﴿٢١﴾
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجۡنُونٖ ﰕ ﴿٢٢﴾
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
وَلَقَدۡ رَءَاهُ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡمُبِينِ ﰖ ﴿٢٣﴾
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
وَمَا هُوَ عَلَى ٱلۡغَيۡبِ بِضَنِينٖ ﰗ ﴿٢٤﴾
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٖ ﰘ ﴿٢٥﴾
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
فَأَيۡنَ تَذۡهَبُونَ ﰙ ﴿٢٦﴾
إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ ﰚ ﴿٢٧﴾
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَسۡتَقِيمَ ﰛ ﴿٢٨﴾
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ ﰜ ﴿٢٩﴾
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.