Hausa
Surah Al-Infitar ( The Cleaving ) - Aya count 19
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتۡ ﰀ ﴿١﴾
وَإِذَا ٱلۡكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتۡ ﰁ ﴿٢﴾
Kuma idan taurãri suka wãtse.
وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ فُجِّرَتۡ ﰂ ﴿٣﴾
Kuma idan tẽkuna aka facce su.
وَإِذَا ٱلۡقُبُورُ بُعۡثِرَتۡ ﰃ ﴿٤﴾
Kuma idan kaburbura aka tõne su.
عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّا قَدَّمَتۡ وَأَخَّرَتۡ ﰄ ﴿٥﴾
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
يَٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلۡكَرِيمِ ﰅ ﴿٦﴾
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ ﰆ ﴿٧﴾
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ ﰇ ﴿٨﴾
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
كَلَّا بَلۡ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ ﰈ ﴿٩﴾
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
وَإِنَّ عَلَيۡكُمۡ لَحَٰفِظِينَ ﰉ ﴿١٠﴾
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
كِرَامٗا كَٰتِبِينَ ﰊ ﴿١١﴾
يَعۡلَمُونَ مَا تَفۡعَلُونَ ﰋ ﴿١٢﴾
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ ﰌ ﴿١٣﴾
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ ﰍ ﴿١٤﴾
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ ﰎ ﴿١٥﴾
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ ﰏ ﴿١٦﴾
Bã zã su faku daga gare ta ba.
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ ﰐ ﴿١٧﴾
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?
ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ ﰑ ﴿١٨﴾
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ ﰒ ﴿١٩﴾
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.