Hausa
Surah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Aya count 25
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتۡ ﰀ ﴿١﴾
وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ ﰁ ﴿٢﴾
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا ٱلۡأَرۡضُ مُدَّتۡ ﰂ ﴿٣﴾
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلۡقَتۡ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتۡ ﰃ ﴿٤﴾
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ ﰄ ﴿٥﴾
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدۡحٗا فَمُلَٰقِيهِ ﰅ ﴿٦﴾
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ ﰆ ﴿٧﴾
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوۡفَ يُحَاسَبُ حِسَابٗا يَسِيرٗا ﰇ ﴿٨﴾
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورٗا ﰈ ﴿٩﴾
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهۡرِهِۦ ﰉ ﴿١٠﴾
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوۡفَ يَدۡعُواْ ثُبُورٗا ﰊ ﴿١١﴾
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصۡلَىٰ سَعِيرًا ﰋ ﴿١٢﴾
إِنَّهُۥ كَانَ فِيٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورًا ﰌ ﴿١٣﴾
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ ﰍ ﴿١٤﴾
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَىٰٓۚ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرٗا ﰎ ﴿١٥﴾
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلشَّفَقِ ﰏ ﴿١٦﴾
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَٱلَّيۡلِ وَمَا وَسَقَ ﰐ ﴿١٧﴾
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَٱلۡقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ ﰑ ﴿١٨﴾
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرۡكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٖ ﰒ ﴿١٩﴾
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ ﰓ ﴿٢٠﴾
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقُرۡءَانُ لَا يَسۡجُدُونَۤ۩ ﰔ ﴿٢١﴾
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَ ﰕ ﴿٢٢﴾
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُوعُونَ ﰖ ﴿٢٣﴾
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرۡهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ ﰗ ﴿٢٤﴾
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ لَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونِۭ ﰘ ﴿٢٥﴾
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.