Hausa
Surah Al-Balad ( The City ) - Aya count 20
لَآ أُقۡسِمُ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ﰀ ﴿١﴾
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ﰁ ﴿٢﴾
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٖ وَمَا وَلَدَ ﰂ ﴿٣﴾
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِي كَبَدٍ ﰃ ﴿٤﴾
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحۡسَبُ أَن لَّن يَقۡدِرَ عَلَيۡهِ أَحَدٞ ﰄ ﴿٥﴾
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا ﰅ ﴿٦﴾
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ ﰆ ﴿٧﴾
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَيۡنَيۡنِ ﰇ ﴿٨﴾
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانٗا وَشَفَتَيۡنِ ﰈ ﴿٩﴾
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ ﰉ ﴿١٠﴾
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ ﰊ ﴿١١﴾
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ ﰋ ﴿١٢﴾
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍ ﰌ ﴿١٣﴾
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ ﰍ ﴿١٤﴾
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ ﰎ ﴿١٥﴾
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ ﰏ ﴿١٦﴾
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ ﰐ ﴿١٧﴾
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُوْلَٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ ﰑ ﴿١٨﴾
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ ﰒ ﴿١٩﴾
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ ﰓ ﴿٢٠﴾
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.