Hausa
Surah Al-Layl ( The Night ) - Aya count 21
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ ﰀ ﴿١﴾
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ ﰁ ﴿٢﴾
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ ﰂ ﴿٣﴾
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ ﰃ ﴿٤﴾
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنۡ أَعۡطَىٰ وَٱتَّقَىٰ ﰄ ﴿٥﴾
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ ﰅ ﴿٦﴾
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡيُسۡرَىٰ ﰆ ﴿٧﴾
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ ﰈ ﴿٩﴾
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ ﰉ ﴿١٠﴾
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغۡنِي عَنۡهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ ﰊ ﴿١١﴾
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ ﰋ ﴿١٢﴾
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ ﰌ ﴿١٣﴾
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرۡتُكُمۡ نَارٗا تَلَظَّىٰ ﰍ ﴿١٤﴾
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصۡلَىٰهَآ إِلَّا ٱلۡأَشۡقَى ﰎ ﴿١٥﴾
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
ٱلَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ﰏ ﴿١٦﴾
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلۡأَتۡقَى ﰐ ﴿١٧﴾
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
ٱلَّذِي يُؤۡتِي مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ ﰑ ﴿١٨﴾
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعۡمَةٖ تُجۡزَىٰٓ ﰒ ﴿١٩﴾
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ رَبِّهِ ٱلۡأَعۡلَىٰ ﰓ ﴿٢٠﴾
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوۡفَ يَرۡضَىٰ ﰔ ﴿٢١﴾
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).