Hausa
Surah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) - Aya count 11
وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ ﰁ ﴿٢﴾
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ ﰂ ﴿٣﴾
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ ﰃ ﴿٤﴾
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ ﰄ ﴿٥﴾
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ ﰅ ﴿٦﴾
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ ﰆ ﴿٧﴾
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ ﰈ ﴿٩﴾
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ ﰉ ﴿١٠﴾
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ ﰊ ﴿١١﴾
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).