Hausa
Surah As-Sharh ( The Opening Forth) - Aya count 8
أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ ﰀ ﴿١﴾
Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?
وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ ﰁ ﴿٢﴾
Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.
ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ ﰂ ﴿٣﴾
Wanda ya nauyayi bãyanka?
وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ ﰃ ﴿٤﴾
Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?
فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا ﰄ ﴿٥﴾
To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا ﰅ ﴿٦﴾
Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ ﰆ ﴿٧﴾
Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب ﰇ ﴿٨﴾
Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.