The best companion that never bores
Surah Az-Zalzalah ( The Earthquake )

Hausa

Surah Az-Zalzalah ( The Earthquake ) - Aya count 8

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا ﰀ ﴿١﴾

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا ﰁ ﴿٢﴾

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا ﰂ ﴿٣﴾

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا ﰃ ﴿٤﴾

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا ﰄ ﴿٥﴾

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ ﰅ ﴿٦﴾

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ ﰆ ﴿٧﴾

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ ﰇ ﴿٨﴾

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.