Hausa
Surah Az-Zalzalah ( The Earthquake ) - Aya count 8
إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا ﰀ ﴿١﴾
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا ﰁ ﴿٢﴾
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا ﰂ ﴿٣﴾
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا ﰃ ﴿٤﴾
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا ﰄ ﴿٥﴾
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ ﰅ ﴿٦﴾
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ ﰆ ﴿٧﴾
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ ﰇ ﴿٨﴾
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.